< Zabura 87 >
1 Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
Su cimiento es en montes de santidad.
2 Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
Ama Jehová las puertas de Sión, más que todas las moradas de Jacob.
3 Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
Cosas ilustres son dichas de ti, ciudad de Dios. (Selah)
4 “Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
Yo me acordaré de Rahab y de Babilonia, entre los que me conocen: he aquí Palestina, y Tiro, con Etiopía: este nació allá.
5 Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
Y de Sión se dirá: Este, y aquel es nacido en ella: y el mismo Altísimo la fortificará.
6 Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
Jehová contará, cuando se escribieren los pueblos: Este nació allí. (Selah)
7 Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”
Y cantores con músicos de flautas: todas mis fuentes estarán en ti.