< Zabura 87 >

1 Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
Von den Korahiten ein Psalm, ein Lied.
2 Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
lieb hat der HERR die Tore Zions mehr als alle (anderen) Wohnstätten Jakobs.
3 Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
Herrliches ist von dir berichtet, du Gottesstadt. (SELA)
4 “Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
»Ich nenne Ägypten und Babel als meine Bekenner, hier das Philisterland und Tyrus samt Äthiopien – nämlich wer dort seine Heimat hat.«
5 Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
Doch von Zion heißt es: »Mann für Mann hat dort seine Heimat, und er selbst, der Höchste, macht es stark.«
6 Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
Der HERR zählt, wenn er die Völker aufschreibt: »Dieser hat dort seine Heimat.« (SELA)
7 Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”
Sie aber tanzen den Reigen und singen: »Alle meine Quellen sind in dir (o Zion)!«

< Zabura 87 >