< Zabura 87 >

1 Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
Cantique des fils de Coré. Il a sa résidence sur les montagnes saintes;
2 Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
l'Éternel aime les portes de Sion plus que toutes les demeures de Jacob.
3 Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
Il est dit de toi des choses glorieuses, Cité de Dieu! (Pause)
4 “Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
« Je me vois reconnu par l'Egypte et Babel; voici, la Philistie, et Tyr avec l'Ethiopie, les uns et les autres reçoivent dans Sion une [nouvelle] naissance. »
5 Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
Et il est dit de Sion: « Des hommes et des hommes y reçoivent une [nouvelle] naissance, et Lui-même, le Très-haut, la consolide. »
6 Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
L'Éternel énumère les peuples en les inscrivant: « Ceux-ci reçoivent là une [nouvelle] naissance. (Pause)
7 Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”
Et les chantres, et les danseurs [s'écrient: ] « Toutes mes sources sont en toi. »

< Zabura 87 >