< Zabura 87 >

1 Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
The city that Yahweh established is on his sacred hill.
2 Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
He loves that city, Jerusalem, more than he loves any other city in Israel.
3 Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
[You people in] [APO] the city that God (owns/lives in), people say wonderful things about your city.
4 “Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
[Some of those who know about God are the people of] Egypt and Babylonia, and also [the people of] Philistia and Tyre and Ethiopia; [some day they all] will say, “[Although I was not born in Jerusalem], [because I belong to Yahweh, it is as though] I was born there.”
5 Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
And concerning Jerusalem, people will say [“It is as though] everyone was born there, and Almighty God will cause that city to remain strong/safe/secure.”
6 Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
Yahweh will write a list of [the names of] the people of various groups [who belong to him], and he will say that [he considers them] all to be citizens of Jerusalem.
7 Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”
They will all dance and sing, saying, “Jerusalem is the source of all our blessings.”

< Zabura 87 >