< Zabura 87 >
1 Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
“By the sons of Korach; a psalm or song.” It is founded by him on holy mountains.
2 Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
The Lord loveth the gates of Zion more than all the dwellings of Jacob.
3 Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
Glorious things are spoken of thee, O city of God. (Selah)
4 “Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
I will make mention of Rahab and Babylon as those that know me; behold, here is Philistia, and Tyre, with Ethiopia: “This man was born there.”
5 Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
But of Zion will it be said, “This and that man were born in her:” and the Most High himself doth establish her.
6 Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
The Lord will number when he writeth down nations. “This man was born there.” (Selah)
7 Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”
And the singers as well as the players on instruments shall be there: all my springs [of joy] are in thee.