< Zabura 87 >
1 Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
A Psalm of the sons of Korah. A song. He has founded His city on the holy mountains.
2 Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
The LORD loves the gates of Zion more than all the dwellings of Jacob.
3 Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
Glorious things are ascribed to you, O city of God.
4 “Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
“I will mention Rahab and Babylon among those who know Me— along with Philistia, Tyre, and Cush — when I say, ‘This one was born in Zion.’”
5 Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
And it will be said of Zion: “This one and that one were born in her, and the Most High Himself will establish her.”
6 Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
The LORD will record in the register of the peoples: “This one was born in Zion.”
7 Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”
Singers and pipers will proclaim, “All my springs of joy are in You.”