< Zabura 86 >

1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
Молитва Давидова.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Бережи мою душу, бо я богобі́йний, спаси Ти, мій Боже, Свого раба, що на Тебе наді́ю кладе́!
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Змилосе́рдься до мене, о Господи, бо я кличу до Тебе ввесь день,
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
потіш душу Свого раба, бо до Тебе підно́шу я, Господи, душу мою,
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
бо Ти, Господи, добрий і вибачли́вий, і многомилости́вий для всіх, хто кли́че до Тебе!
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Почуй же, о Господи, молитву мою, і вислухай голос блага́ння мого, —
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
в день недолі своєї я кличу до Тебе, бо Ти обізве́шся до мене!
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
Нема, Господи, поміж бога́ми такого, як Ти, і чинів нема, як чи́ни Твої!
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
Всі наро́ди, яких Ти створи́в, поприхо́дять і попадають перед лице́м Твоїм, Господи, та Ім'я́ Твоє сла́вити будуть,
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
великий бо Ти, та чу́да вчиняєш, Ти — Бог єдиний!
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Дорогу Свою покажи мені, Господи, і я бу́ду ходити у правді Твоїй, приєдна́й моє серце боятися Йме́ння Твого́!
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
Я буду всім серцем своїм вихваля́ти Тебе, Господи, Боже Ти мій, і сла́вити буду повіки Ім'я́ Твоє,
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
велика бо милість Твоя надо мною, і вирвав Ти душу мою від шео́лу глибокого! (Sheol h7585)
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
Боже, злочинці повстали на мене, а на́товп гноби́телів прагне моєї душі, і перед собою не ставлять Тебе.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
А Ти, Господи, Бог щедрий і милосердний, довготерпели́вий і многомилости́вий, і справедли́вий, —
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
зглянься на мене, й помилуй мене, подай же Своєму рабові Свою силу, і спаси сина Своєї неві́льниці!
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Учини мені знака на добре, — і нехай це побачать мої ненави́сники, і хай засоро́млені будуть, бо Ти, Господи, мені допоміг та мене звесели́в!

< Zabura 86 >