< Zabura 86 >

1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
Davut'un duası Kulak ver, ya RAB, yanıtla beni, Çünkü mazlum ve yoksulum.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Koru canımı, çünkü senin sadık kulunum. Ey Tanrım, kurtar sana güvenen kulunu!
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Acı bana, ya Rab, Çünkü gün boyu sana yakarıyorum.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Sevindir kulunu, ya Rab, Çünkü dualarımı sana yükseltiyorum.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
Sen iyi ve bağışlayıcısın, ya Rab, Sana yakaran herkese bol sevgi gösterirsin.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Kulak ver duama, ya RAB, Yalvarışlarımı dikkate al!
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
Sıkıntılı günümde sana yakarırım, Çünkü yanıtlarsın beni.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
İlahlar arasında senin gibisi yok, ya Rab, Eşsizdir işlerin.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
Yarattığın bütün uluslar gelip Sana tapınacaklar, ya Rab, Adını yüceltecekler.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
Çünkü sen ulusun, harikalar yaratırsın, Tek Tanrı sensin.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Ya RAB, yolunu bana öğret, Senin gerçeğine göre yürüyeyim, Kararlı kıl beni, yalnız senin adından korkayım.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
Ya Rab Tanrım, bütün yüreğimle sana şükredeceğim, Adını sonsuza dek yücelteceğim.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
Çünkü bana sevgin büyüktür, Canımı ölüler diyarının derinliklerinden sen kurtardın. (Sheol h7585)
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
Ey Tanrı, küstahlar bana saldırıyor, Zorbalar sürüsü, sana aldırmayanlar Canımı almak istiyor,
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
Oysa sen, ya Rab, Sevecen, lütfeden, tez öfkelenmeyen, Sevgisi ve sadakati bol bir Tanrı'sın.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Yönel bana, acı halime, Kuluna kendi gücünü ver, Kurtar hizmetçinin oğlunu.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
İyiliğinin bir belirtisini göster bana; Benden nefret edenler görüp utansın; Çünkü sen, ya RAB, bana yardım ettin, Beni avuttun.

< Zabura 86 >