< Zabura 86 >

1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
MAIN Ieowa, kom kotin kapaike don ia karon omui kan o mani ia, pwe nai me luet o jamama.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Kom kotin apali maur i, pwe nai me lelapok. Main Kot, kom kotin jauaja ia, japwilim omui ladu men et, me liki komui.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Main, kom kotin maki on ia, pwe i kin likwir on komui ni anjau karoj.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Kom kotin kaperenda monion en japwilim omui ladu, pwe monion i kin anane komui Main.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
Pwe komui Main me mau o kalanan, o kom kotin kalanan on ir karoj, me kin likwir on komui.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Main Ieowa, kom kotin ereki ai kapakap, o kotin mani nil en ai nidinid.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
Ni ai apwal akan i kin likwir on komui, pwe kom, kotin mani ia!
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
Main, jota me dueta komui nan pun en kot akan; o jota me kak wiawia dueta komui.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
Men liki kan karoj pan pwarado, pwen kaudoki on komui Main, o wauneki mar omui.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
Pwe komui me lapalap, me kin wiada manaman, o komui ta me Kot.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Main Ieowa, re kotin kajale on ia al omui, pwe i en weweid ni omui melel, kom kotin kolekol monion i on iet eta: Majak mar omui.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
I men kapina komui Main, ai Kot, jan nan monion i, o wauneki mar omui kokolata.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
Pwe omui kalanan me laud on ia; komui dore maur i jan nan wajan mela. (Sheol h7585)
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
Main Kot, me aklapalap akan kin palian ia, o pwin en me weit akan kin majamajan maur i, o re jota kin weweid mon jilan omui.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
A komui Main Kot, me dir en kalanan, o mak, o kanonama, o omui kapunlol o melel me lapalap.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Kom kotin wukidoki don ia, o maki on ia, o kamaui kida japwilim omui ladu omui manaman, o kotin jauaja nain japwilim omui lidu!
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Kom kotiki on ia kilel eu, me i pan paie kida, pwe ai imwintiti kan en kilan, rap namenok kila omui kotin jauaja ia, Main Ieowa, o kom kotin kamait ia la.

< Zabura 86 >