< Zabura 86 >
1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
Prière de David. Éternel, prête l’oreille, exauce-moi! Car je suis malheureux et indigent.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Garde mon âme, car je suis pieux! Mon Dieu, sauve ton serviteur qui se confie en toi!
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Aie pitié de moi, Seigneur! Car je crie à toi tout le jour.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Réjouis l’âme de ton serviteur, Car à toi, Seigneur, j’élève mon âme.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
Car tu es bon, Seigneur, tu pardonnes, Tu es plein d’amour pour tous ceux qui t’invoquent.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Éternel, prête l’oreille à ma prière, Sois attentif à la voix de mes supplications!
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
Je t’invoque au jour de ma détresse, Car tu m’exauces.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
Nul n’est comme toi parmi les dieux, Seigneur, Et rien ne ressemble à tes œuvres.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
Toutes les nations que tu as faites viendront Se prosterner devant ta face, Seigneur, Et rendre gloire à ton nom.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
Car tu es grand, et tu opères des prodiges; Toi seul, tu es Dieu.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Enseigne-moi tes voies, ô Éternel! Je marcherai dans ta fidélité. Dispose mon cœur à la crainte de ton nom.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
Je te louerai de tout mon cœur, Seigneur, mon Dieu! Et je glorifierai ton nom à perpétuité.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
Car ta bonté est grande envers moi, Et tu délivres mon âme du séjour profond des morts. (Sheol )
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
O Dieu! des orgueilleux se sont levés contre moi, Une troupe d’hommes violents en veulent à ma vie; Ils ne portent pas leurs pensées sur toi.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
Mais toi, Seigneur, tu es un Dieu miséricordieux et compatissant, Lent à la colère, riche en bonté et en fidélité;
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Tourne vers moi les regards et aie pitié de moi, Donne la force à ton serviteur, Et sauve le fils de ta servante!
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Opère un signe en ma faveur! Que mes ennemis le voient et soient confus! Car tu me secours et tu me consoles, ô Éternel!