< Zabura 86 >

1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
A prayer of David incline O Yahweh ear your answer me for [am] poor and needy I.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Preserve! life my for [am] faithful I save servant your you [are] God my who trusts to you.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Show favor to me O Lord for to you I call out all the day.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Make glad [the] self of servant your for to you O Lord being my I lift up.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
For you O Lord [are] good and ready to forgive and great of covenant loyalty to all [those who] call out to you.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Give ear to! O Yahweh prayer my and pay attention! to [the] sound of supplications my.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
On [the] day of distress my I call out to you for you will answer me.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
There not [is] like you among the gods - O Lord and there not [are] like works your.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
All [the] nations - which you have made they will come - and they may bow down before you O Lord so they may glorify name your.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
For [are] great you and [one who] does wonders you [are] God to alone you.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Teach me O Yahweh - way your I will walk in truth your unite heart my to fear name your.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
I will give thanks to you - O Lord God my with all heart my and I will glorify name your for ever.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
For covenant loyalty your [is] great towards me and you have delivered life my from Sheol lowest. (Sheol h7585)
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
O God - arrogant [people] they have risen up on me and a company of ruthless [people] they have sought life my and not they have set you to before themselves.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
And you O Lord [are] a God compassionate and gracious long of anger and great of covenant loyalty and faithfulness.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Turn to me and show favor to me give! strength your to servant your and save! [the] son of maidservant your.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Do with me a sign of goodness so they may see [those who] hate me and they may be ashamed for you O Yahweh you have helped me and you have comforted me.

< Zabura 86 >