< Zabura 86 >
1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
A prayer of David. Incline your ear, Lord, and answer me, for I am afflicted and needy.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Guard me, for I am loyal: save your servant, who trusts in you.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Lord, be gracious to me, for you are my God; I cry to you all the day.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Gladden the heart of your servant; for to you, Lord, I set my hope.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
For you, Lord, are good and forgiving, rich in love towards all who call on you.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Listen, O Lord, to my prayer; attend to my plea for mercy.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
In the day of my trouble I call on you, with assurance that you will answer me.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
None of the gods is like you, Lord, nor are any works like yours.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
All the nations you have made will come and bow down before you, giving glory, O Lord, to your name.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
For great are you, and a doer of wonders; you alone are God.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Teach me, O Lord, your way, that I may walk in your truth: so my heart shall rejoice in your name.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
I will give you thanks, O Lord, with all my heart, my God, I will honor your name forever.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
For great is your love towards me, from the depths of Sheol you have saved me. (Sheol )
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
Haughty men have risen up against me, O God, a band of the violent seeking my life, who think nothing of you.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
But you are a God of pity and grace, patient and rich in kindness and faithfulness; turn to me with your grace, O Lord.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Grant your strength to your servant, and save the child of your handmaid.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Show me a sign of your favor, which those who hate me may see with confusion, since you, Lord, are my helper and comforter.