< Zabura 86 >
1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
A PRAYER OF DAVID. Incline, O YHWH, Your ear, Answer me, for I [am] poor and needy.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Keep my soul, for I [am] pious, Save Your servant who is trusting to You, O You, my God.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Favor me, O Lord, for I call to You all the day.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Make glad the soul of Your servant, For to You, O Lord, I lift up my soul.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
For You, Lord, [are] good and forgiving, And abundant in kindness to all calling You.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Hear, O YHWH, my prayer, And attend to the voice of my supplications.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
In a day of my distress I call You, For You answer me.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
There is none like You among the gods, O Lord, And like Your works there are none.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
All nations that You have made Come and bow themselves before You, O Lord, And give honor to Your Name.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
For You [are] great, and doing wonders, You [are] God alone.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Show me, O YHWH, Your way, I walk in Your truth, My heart rejoices to fear Your Name.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
I confess You, O Lord my God, with all my heart, And I honor Your Name for all time.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
For Your kindness [is] great toward me, And You have delivered my soul from the lowest Sheol. (Sheol )
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
O God, the proud have risen up against me, And a company of the terrible sought my soul, And have not placed You before them,
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
And You, O Lord, [are] God, merciful and gracious, Slow to anger, and abundant in kindness and truth.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Look to me, and favor me, Give Your strength to Your servant, And give salvation to a son of Your handmaid.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Do with me a sign for good, And those hating me see and are ashamed, For You, O YHWH, have helped me, Indeed, You have comforted me!