< Zabura 86 >
1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
Bow down your ear, O LORD, hear me: for I am poor and needy.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Preserve my soul; for I am holy: O you my God, save your servant that trusts in you.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Be merciful to me, O Lord: for I cry to you daily.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Rejoice the soul of your servant: for to you, O Lord, do I lift up my soul.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
For you, Lord, are good, and ready to forgive; and plenteous in mercy to all them that call on you.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Give ear, O LORD, to my prayer; and attend to the voice of my supplications.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
In the day of my trouble I will call on you: for you will answer me.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
Among the gods there is none like to you, O Lord; neither are there any works like to your works.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
All nations whom you have made shall come and worship before you, O Lord; and shall glorify your name.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
For you are great, and do wondrous things: you are God alone.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Teach me your way, O LORD; I will walk in your truth: unite my heart to fear your name.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
I will praise you, O Lord my God, with all my heart: and I will glorify your name for ever more.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
For great is your mercy toward me: and you have delivered my soul from the lowest hell. (Sheol )
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
O God, the proud are risen against me, and the assemblies of violent men have sought after my soul; and have not set you before them.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
But you, O Lord, are a God full of compassion, and gracious, long suffering, and plenteous in mercy and truth.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
O turn to me, and have mercy on me; give your strength to your servant, and save the son of your handmaid.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Show me a token for good; that they which hate me may see it, and be ashamed: because you, LORD, have helped me, and comforted me.