< Zabura 86 >
1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
A Prayer of David. Incline Thine ear, O LORD, and answer me; for I am poor and needy.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Keep my soul, for I am godly; O Thou my God, save Thy servant that trusteth in Thee.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Be gracious unto me, O Lord; for unto Thee do I cry all the day.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Rejoice the soul of Thy servant; for unto Thee, O Lord, do I lift up my soul.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
For Thou, Lord, art good, and ready to pardon, and plenteous in mercy unto all them that call upon Thee.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Give ear, O LORD, unto my prayer; and attend unto the voice of my supplications.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
In the day of my trouble I call upon Thee; for Thou wilt answer me.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
There is none like unto Thee among the gods, O Lord, and there are no works like Thine.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
All nations whom Thou hast made shall come and prostrate themselves before Thee, O Lord; and they shall glorify Thy name.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
For Thou art great, and doest wondrous things; Thou art God alone.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Teach me, O LORD, Thy way, that I may walk in Thy truth; make one my heart to fear Thy name.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
I will thank Thee, O Lord my God, with my whole heart; and I will glorify Thy name for evermore.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
For great is Thy mercy toward me; and Thou hast delivered my soul from the lowest nether-world. (Sheol )
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
O God, the proud are risen up against me, and the company of violent men have sought after my soul, and have not set Thee before them.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
But Thou, O Lord, art a God full of compassion and gracious, slow to anger, and plenteous in mercy and truth.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
O turn unto me, and be gracious unto me; give Thy strength unto Thy servant, and save the son of Thy handmaid.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Work in my behalf a sign for good; that they that hate me may see it, and be put to shame, because Thou, LORD, hast helped me, and comforted me.