< Zabura 86 >

1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
A prayer of David. Please listen to me, Lord! Please answer me, for I am weak and really need your help!
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Don't let me die, for I am faithful to you. Save me, for I am your servant and I trust in you. You are my God.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Be kind to me, Lord, for I call out to you all day long.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Make me happy, Lord, for I've dedicated my life to you.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
For you, Lord, are good; you are forgiving and full of trustworthy love for all who come to you.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Lord, please listen to my prayer. Hear my call for help.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
When I'm in trouble I cry out to you because I know you will answer me.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
There's no one like you among the “gods,” Lord. No one can do the things you do.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
You created all the nations, and they will come and bow down before you, Lord. They will declare how wonderful you are.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
For you are great, and do wonderful things! Only you are God.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Lord, please teach me your way, so I can depend on your trustworthiness. Make me single-minded, so I can consistently honor the kind of person you are.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
Lord my God, I thank you from the bottom of my heart. I will praise your character forever.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
For your trustworthy love for me is so great; you have saved me from death. (Sheol h7585)
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
God, arrogant people are attacking me, vicious people are trying to kill me. To them you count for nothing.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
But you, Lord, are a compassionate and gracious God, slow to become angry, full of trustworthy love and faithfulness.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Turn to me, have mercy on me. Give me your strength, your servant; save the son of your servant-girl.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Show me a sign that you approve of me! Those who hate me will see it, and they will be ashamed because you, Lord, have helped me.

< Zabura 86 >