< Zabura 86 >
1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
A Prayer of David himself. Incline your ear, O Lord, and hear me. For I am needy and poor.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Preserve my soul, for I am holy. My God, bring salvation to your servant who hopes in you.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
O Lord, be merciful to me, for I have cried out to you all day long.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Give joy to the soul of your servant, for I have lifted up my soul to you, Lord.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
For you are sweet and mild, Lord, and plentiful in mercy to all who call upon you.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Pay attention, Lord, to my prayer, and attend to the voice of my supplication.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
In the day of my tribulation, I cried out to you, because you heeded me.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
There is no one like you among the gods, O Lord, and there is no one like you in your works.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
All the nations, which you have made, will draw near and adore in your presence, O Lord. And they will glorify your name.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
For you are great, and you perform wonders. You alone are God.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Lead me, O Lord, in your way, and I will walk in your truth. May my heart rejoice, so that it will fear your name.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
I will confess to you, O Lord my God, with my whole heart. And I will glorify your name in eternity.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
For your mercy toward me is great, and you have rescued my soul from the lower part of Hell. (Sheol )
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
O God, the iniquitous have risen up against me, and the synagogue of the powerful have sought my soul, and they have not placed you in their sight.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
And you, Lord God, are compassionate and merciful, being patient and full of mercy and truthful.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Look down upon me and have mercy on me. Grant your authority to your servant, and bring salvation to the son of your handmaid.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Make me a sign of what is good, so that those who hate me, may look and be confounded. For you, O Lord, have helped me and consoled me.