< Zabura 86 >
1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
Modlitba Davidova. Nakloň, Hospodine, ucha svého, a vyslyš mne, neboť jsem chudý a nuzný.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Ostříhejž duše mé, neboť jsem ten, jehož miluješ; zachovej služebníka svého, ty Bože můj, v tobě naději majícího.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Smiluj se nade mnou, Hospodine, k toběť zajisté každého dne volám.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Potěš duše služebníka svého, neboť k tobě, ó Pane, duše své pozdvihuji.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
Nebo ty jsi, Pane, dobrotivý a lítostivý, a hojný v milosrdenství ke všechněm, kteříž tě vzývají.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Slyš, Hospodine, modlitbu mou, a pozoruj hlasu žádostí mých.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
V den ssoužení svého vzývám tě, nebo mne vyslýcháš.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
Neníť žádného tobě podobného mezi bohy, ó Pane, a není takových skutků, jako jsou tvoji.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
Všickni národové, kteréž jsi učinil, přicházejíce, skláněti se budou před tebou, Pane, a ctíti jméno tvé.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
Nebo jsi ty veliký, a činíš divné věci, ty jsi Bůh sám.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Vyuč mne, Hospodine, cestě své, abych chodil v pravdě tvé; ustav srdce mé v bázni jména svého.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
I budu tě oslavovati, Pane Bože můj, z celého srdce svého a ctíti jméno tvé na věky,
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
Poněvadž milosrdenství tvé veliké jest nade mnou, a vytrhls duši mou z jámy nejhlubší. (Sheol )
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
Ó Bože, povstaliť jsou pyšní proti mně, a rota násilníků hledají bezživotí mého, ti, kteříž tě sobě nepředstavují.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
Ale ty Pane, Bože silný, lítostivý a milostivý, shovívající a hojný v milosrdenství, i pravdomluvný,
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Vzhlédniž na mne, a smiluj se nade mnou, obdař silou svou služebníka svého, a zachovávej syna děvky své.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Prokaž ke mně znamení dobrotivosti, tak aby vidouce to ti, kteříž mne nenávidí, zahanbeni byli, že jsi ty mi, Hospodine, spomohl, a mne potěšil.