< Zabura 84 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
Müzik şefi için - Gittit üzerine - Korahoğulları'nın mezmuru Ey Her Şeye Egemen RAB, Ne kadar severim konutunu!
2 Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
Canım senin avlularını özlüyor, İçim çekiyor, Yüreğim, bütün varlığım Sana, yaşayan Tanrı'ya sevinçle haykırıyor.
3 Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
Kuşlar bile bir yuva, Kırlangıç, yavrularını koyacak bir yer buldu Senin sunaklarının yanında, Ey Her Şeye Egemen RAB, Kralım ve Tanrım!
4 Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
Ne mutlu senin evinde oturanlara, Seni sürekli överler! (Sela)
5 Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
Ne mutlu gücünü senden alan insana! Aklı hep Siyon'u ziyaret etmekte.
6 Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
Baka Vadisi'nden geçerken, Pınar başına çevirirler orayı, İlk yağmurlar orayı berekete boğar.
7 Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
Gittikçe güçlenir, Siyon'da Tanrı'nın huzuruna çıkarlar.
8 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Ya RAB, Her Şeye Egemen Tanrı, duamı dinle, Kulak ver, ey Yakup'un Tanrısı! (Sela)
9 Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
Ey Tanrı, kalkanımıza bak, Meshettiğin krala lütfet!
10 Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
Senin avlularında bir gün, Başka yerdeki bin günden iyidir; Kötülerin çadırında yaşamaktansa, Tanrım'ın evinin eşiğinde durmayı yeğlerim.
11 Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
Çünkü RAB Tanrı bir güneş, bir kalkandır. Lütuf ve yücelik sağlar; Dürüstçe yaşayanlardan hiçbir iyiliği esirgemez.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.
Ey Her Şeye Egemen RAB, Ne mutlu sana güvenen insana!

< Zabura 84 >