< Zabura 84 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
Veisuunjohtajalle; veisataan kuin viininkorjuulaulu; koorahilaisten virsi. Kuinka ihanat ovat sinun asuinsijasi, Herra Sebaot!
2 Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
Minun sieluni ikävöitsee ja halajaa Herran esikartanoihin, minun sydämeni ja ruumiini pyrkii riemuiten elävää Jumalaa kohti.
3 Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
Löysihän lintunen majan ja pääskynen pesän, johon se poikasensa laskee: sinun alttarisi, Herra Sebaot, minun kuninkaani ja minun Jumalani.
4 Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
Autuaat ne, jotka sinun huoneessasi asuvat! He kiittävät sinua alati. (Sela)
5 Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
Autuaat ne ihmiset, joilla on voimansa sinussa, joilla on mielessänsä pyhät matkat!
6 Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
Kun he käyvät Kyynellaakson kautta, he muuttavat sen lähteitten maaksi, ja syyssade peittää sen siunauksilla.
7 Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
He käyvät voimasta voimaan, he astuvat Jumalan eteen Siionissa.
8 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Herra, Jumala Sebaot, kuule minun rukoukseni, ota se korviisi, Jaakobin Jumala. (Sela)
9 Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
Jumala, meidän kilpemme, käännä katseesi, katso voideltusi kasvoja.
10 Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
Sillä yksi päivä sinun esikartanoissasi on parempi kuin tuhat muualla; mieluummin minä olen vartijana Jumalani huoneen kynnyksellä, kuin asun jumalattomien majoissa.
11 Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
Sillä Herra Jumala on aurinko ja kilpi; Herra antaa armon ja kunnian, ei hän kiellä hyvää niiltä, jotka nuhteettomasti vaeltavat.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.
Herra Sebaot, autuas se ihminen, joka sinuun turvaa!

< Zabura 84 >