< Zabura 84 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
Koran lasten Psalmi, Gittitin päällä, edelläveisaajalle. Kuinka ihanat ovat sinun asuinsijas, Herra Zebaot!
2 Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
Minun sieluni ikävöitsee ja halajaa Herran esikartanoihin: minun ruumiini ja sieluni iloitsee elävässä Jumalassa.
3 Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
Sillä lintu on huoneen löytänyt, ja pääskynen pesänsä, johonka he poikansa laskevat: sinun alttaris, Herra Zebaot, minun kuninkaani ja minun Jumalani.
4 Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
Autuaat ovat, jotka sinun huoneessas asuvat: he kiittävät sinua ijankaikkisesti, (Sela)
5 Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
Autuaat ovat ne ihmiset, jotka sinun pitävät väkenänsä, ja sydämestänsä vaeltavat sinun jälkees,
6 Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
Jotka käyvät itkun laakson lävitse, ja tekevät siellä kaivoja; ja opettajat monella siunauksella kaunistetaan.
7 Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
He saavat yhden voiton toisen jälkeen, että tunnettaisiin oikia Jumala Zionissa.
8 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Herra Jumala Zebaot, kuule minun rukoukseni: ota, Jakobin Jumala, tätä korviis, (Sela)
9 Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
Katsele siis, Jumala, meidän kilpemme, katso sinun voideltus kasvoja.
10 Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
Sillä yksi päivä esikartanoissas on parempi kuin tuhannen muualla: ennen minä olisin ovenvartia Jumalani huoneessa, kuin asuisin jumalattomain majoissa.
11 Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
Sillä Herra Jumala on aurinko ja kilpi: Herra antaa armon ja kunnian: ei hän anna hurskailta mitään hyvää puuttua.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.
Herra Zebaot, autuas on se ihminen, joka sinuun uskaltaa.