< Zabura 84 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
“For the leader of the music. On the Gittith. A psalm of the sons of Korah.” How lovely are thy tabernacles, O LORD of hosts!
2 Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
My soul longeth, yea, fainteth, for the courts of the LORD; My heart and my flesh cry aloud for the living God.
3 Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
The very sparrow findeth an abode, And the swallow a nest, where they may lay their young, By thine altars, O LORD of hosts, My king and my God!
4 Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
Happy they who dwell in thy house, Who are continually praising thee! (Pause)
5 Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
Happy the man whose glory is in thee, In whose heart are the ways [[to Jerusalem]]!
6 Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
Passing through the valley of Baca, they make it a fountain; and the early rain covereth it with blessings.
7 Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
They go on from strength to strength; Every one of them appeareth before God in Zion.
8 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Hear my prayer, O LORD, God of hosts! Give ear, O God of Jacob! (Pause)
9 Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
Look down, O God! our shield, And behold the face of thine anointed!
10 Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
For a day spent in thy courts is better than a thousand: I would rather stand on the threshold of the house of my God, Than dwell in the tents of wickedness.
11 Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
For the LORD God is a sun and a shield; The LORD giveth grace and glory; No good thing doth he withhold From them that walk uprightly.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.
O LORD of hosts! Happy the man who trusteth in thee!