< Zabura 84 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
For the Leader; upon the Gittith. A Psalm of the sons of Korah. How lovely are Thy tabernacles, O LORD of hosts!
2 Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
My soul yearneth, yea, even pineth for the courts of the LORD; my heart and my flesh sing for joy unto the living God.
3 Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
Yea, the sparrow hath found a house, and the swallow a nest for herself, where she may lay her young; Thine altars, O LORD of hosts, my King, and my God —.
4 Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
Happy are they that dwell in Thy house, they are ever praising Thee. (Selah)
5 Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
Happy is the man whose strength is in Thee; in whose heart are the highways.
6 Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
Passing through the valley of Baca they make it a place of springs; yea, the early rain clotheth it with blessings.
7 Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
They go from strength to strength, every one of them appeareth before God in Zion.
8 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
O LORD God of hosts, hear my prayer; give ear, O God of Jacob. (Selah)
9 Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
Behold, O God our shield, and look upon the face of Thine anointed.
10 Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
For a day in Thy courts is better than a thousand; I had rather stand at the threshold of the house of my God, than to dwell in the tents of wickedness.
11 Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
For the LORD God is a sun and a shield; the LORD giveth grace and glory; no good thing will He withhold from them that walk uprightly.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.
O LORD of hosts, happy is the man that trusteth in Thee.

< Zabura 84 >