< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
En Psalmvisa Assaphs. Gud, tig dock icke så, och var dock icke så stilla; Gud, lid det dock icke så.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Ty si, dine fiender rasa, och de som dig hata, sätta upp hufvudet.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
De hafva listig anslag emot ditt folk, och rådslå emot dina fördolda.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Kommer, säga de, låter oss utrota dem, så att de intet folk äro; att på Israels namn icke skall mer tänkt varda.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Ty de hafva förenat sig med hvarannan, och ett förbund emot dig gjort:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
De Edomeers hyddor, och de Ismaeliters, de Moabiters, och Hagariters,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
De Gebaliters, Ammoniters, och Amalekiters, de Philisteers, samt med dem i Tyro.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Assur hafver ock gifvit sig till dem, och hjelpa Lots barnom. (Sela)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Gör dem såsom de Midianiter, såsom Sisera, såsom Jabin vid den bäcken Kison;
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Hvilke förderfvade vordo vid Endor, och vordo till träck på jordene.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Gör deras Förstar såsom Oreb och Seeb; alle deras öfverstar, såsom Seba och Zalmunna;
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
De der säga: Vi vilje intaga Guds hus.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Min Gud, gör dem såsom en hvärfvel, och såsom strå för väder,
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Såsom en eld, den skog förbränner, och såsom en låga, den berg upptänder.
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Alltså förfölj dem med ditt väder, och förskräck dem med ditt oväder.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Gör deras ansigten fulla med blygd, att de efter ditt Namn. Herre, söka måste;
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Skämme sig, och förskräckes alltid ju mer och mer, och till skam komme, och förgås.
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Så skola de förnimma, att du med ditt Namn heter Herre allena, och den Högste i allo verldene.