< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Wimbo. Zaburi ya Asafu. Ee Mungu, usinyamaze kimya, usinyamaze, Ee Mungu, usitulie.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Tazama watesi wako wanafanya fujo, jinsi adui zako wanavyoinua vichwa vyao.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Kwa hila, wanafanya shauri dhidi ya watu wako, wanafanya shauri baya dhidi ya wale unaowapenda.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Wanasema, “Njooni, tuwaangamize kama taifa, ili jina la Israeli lisikumbukwe tena.”
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Kwa nia moja wanapanga mashauri mabaya pamoja, wanafanya muungano dhidi yako,
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
mahema ya Edomu na Waishmaeli, ya Wamoabu na Wahagari,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebali, Amoni na Amaleki, Ufilisti, pamoja na watu wa Tiro.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Hata Ashuru wameungana nao kuwapa nguvu wazao wa Loti.
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Uwatendee kama vile ulivyowatendea Midiani, na kama vile ulivyowatendea Sisera na Yabini hapo kijito cha Kishoni,
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
ambao waliangamia huko Endori na wakawa kama takataka juu ya nchi.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Wafanye wakuu wao kama Orebu na Zeebu, watawala wao kama Zeba na Salmuna,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
ambao walisema, “Na tumiliki nchi ya malisho ya Mungu.”
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Ee Mungu wangu, wapeperushe kama mavumbi ya kisulisuli, kama makapi yapeperushwayo na upepo.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Kama vile moto uteketezavyo msitu au mwali wa moto unavyounguza milima,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
wafuatilie kwa tufani yako na kuwafadhaisha kwa dhoruba yako.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Funika nyuso zao kwa aibu ili watu walitafute jina lako, Ee Bwana.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Wao na waaibishwe na kufadhaishwa milele, na waangamie kwa aibu.
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Hebu wajue kwamba wewe, ambaye jina lako ni Bwana, kwamba wewe peke yako ndiwe Uliye Juu Sana ya dunia yote.

< Zabura 83 >