< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
O! Dios, no tengas silencio, no calles, ni ceses, o! Dios.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Porque he aquí que tus enemigos han bramado: y tus aborrecedores han alzado cabeza.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Sobre tu pueblo han consultado astuta y secretamente: y han entrado en consejo contra tus escondidos.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Han dicho: Veníd, y cortémoslos de ser nación: y no haya más memoria del nombre de Israel.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Por esto han conspirado de corazón a una: contra ti han hecho liga.
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
Las tiendas de los Idumeos, y de los Ismaelitas: Moab, y los Agarenos;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal, y Ammón, y Amalec: Palestina, con los habitadores de Tiro.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
También el Assur se ha juntado con ellos: son por brazo a los hijos de Lot. (Selah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Házles como a Madián, como a Sisara: como a Jabín en el arroyo de Cisón:
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Que perecieron en En-dor: fueron hechos muladar de la tierra.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Pon a ellos y a sus capitanes como a Oreb, y como a Zeb, y como a Zebee, y como a Salmana: a todos sus príncipes,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
Que han dicho: Heredemos para nosotros las moradas de Dios.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Dios mío, pónlos como a torbellino: como a hojarascas delante del viento:
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Como fuego que quema el monte: como llama que abrasa las breñas;
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Así persíguelos con tu tempestad; y con tu torbellino asómbralos.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Hinche sus rostros de vergüenza; y busquen tu nombre, o! Jehová.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Sean afrentados, y turbados para siempre; y sean deshonrados, y perezcan.
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Y conozcan que tu nombre es Jehová; tú solo Altísimo sobre toda la tierra.

< Zabura 83 >