< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Una canción. Un salmo de Asaf. ¡Por favor, no permanezcas en silencio, Dios! ¡No puedes permanecer inmóvil! Dios, ¡No te quedes callado!
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
¿No escuchas el rugido de tus enemigos? ¿No ves cómo los que te odian levantan sus cabezas desafiantemente?
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Inventan planes astutos para conspirar contra tu pueblo; traman cosas contra los que atesoras.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Dicen, “¡Vamos! Destruyamos su nación para que el nombre ‘Israel’ sea completamente olvidado”.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Todos ellos están de acuerdo en su conspiración; han hecho un trato para atacarte—
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
el pueblo de Edom, los Ismaelitas, Moab, y los ismaelitas;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
el pueblo de Gebal y Ammon y Amalek, Filistea, y los habitantes de Tiro.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Asiria también se les ha unido, se ha aliado con los descendientes de Lot. (Selah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Hazles lo que le hiciste a Madián, lo que le hiciste a Sisera y Jabin y el río Kishon.
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Fueron destruidos en Endor y se convirtieron en estiércol para fertilizar la tierra.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Haz a sus líderes como Oreb y Zeeb; todos sus gobernadores como Zeba y Zalmuna,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
porque ellos dijeron, “¡Tomemos los pastos de Dios para nosotros mismos!”
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Dios mío, hazlos como torbellinos que giran, como pajas arrasadas por el viento.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Como fuego que quema el bosque, como una lama que le prende fuego a las montañas,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
de la misma forma, derríbalos con tu tormenta, aterrorízalos con tu torbellino.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
¡Avergüénzalos con la derrota para que vengan a ti, Señor!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
¡Avergüénzalos! ¡Aterrorízalos para siempre, para que mueran en desgracia!
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Permite que entiendan que solo tú, llamado el Señor, eres el gran Altísimo que rige sobre la tierra.

< Zabura 83 >