< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Cántico. Salmo de Asaf. Oh Dios, no permanezcas mudo; no estés sordo, oh Dios, ni te muestres pasivo.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Mira el tumulto que hacen tus enemigos, y cómo los que te odian yerguen su cabeza.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
A tu pueblo le traman asechanzas; se confabulan contra los que Tú proteges.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
“Venid (dicen), borrémoslos; que ya no sean pueblo; no quede ni memoria del nombre de Israel.”
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Así conspiran todos a una y forman liga contra Ti:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
las tiendas de Edom y los ismaelitas, Moab y los agarenos,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal y Ammón y Amalec, Filistea y los habitantes de Tiro.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
También los asirios se les han unido, y se han hecho auxiliares de los hijos de Lot.
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Haz Tú con ellos como con Madián y con Sísara, y con Jabín, junto al torrente Cisón;
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
que perecieron en Endor, y vinieron a ser como estiércol para la tierra.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Trata a sus caudillos como a Oreb y a Zeb; a todos sus jefes, como a Zebee y a Salmaná,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
pues han dicho: “Ocupemos para nosotros las tierras de Dios.”
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Dios mío, hazlos como el polvo en un remolino y la hojarasca presa del viento.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Como fuego que consume la selva, como llama que abrasa los montes,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
así persíguelos en tu tempestad, y atérralos en tu borrasca.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Haz que sus rostros se cubran de vergüenza, para que busquen tu nombre ¡oh Dios!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Queden para siempre en la ignominia y en la turbación; sean confundidos y perezcan.
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Y sepan que tu Nombre es Yahvé; y que solo Tú eres el Altísimo sobre toda la tierra.