< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Canticum Psalmi Asaph. Deus, quis similis erit tibi? ne taceas, neque compescaris Deus:
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Quoniam ecce inimici tui sonuerunt: et qui oderunt te, extulerunt caput.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Super populum tuum malignaverunt consilium: et cogitaverunt adversus sanctos tuos.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Dixerunt: Venite, et disperdamus eos de gente: et non memoretur nomen Israel ultra.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Quoniam cogitaverunt unanimiter: simul adversum te testamentum disposuerunt,
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
tabernacula Idumæorum et Ismahelitæ: Moab, et Agareni,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal, et Ammon, et Amalec: alienigenæ cum habitantibus Tyrum.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Etenim Assur venit cum illis: facti sunt in adiutorium filiis Lot.
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Fac illis sicut Madian et Sisaræ: sicut Iabin in torrente Cisson.
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Disperierunt in Endor: facti sunt ut stercus terræ.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Pone principes eorum sicut Oreb, et Zeb, et Zebee, et Salmana: Omnes principes eorum:
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
qui dixerunt: Hereditate possideamus Sanctuarium Dei.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Deus meus pone illos ut rotam: et sicut stipulam ante faciem venti.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Sicut ignis, qui comburit silvam: et sicut flamma comburens montes:
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Ita persequeris illos in tempestate tua: et in ira tua turbabis eos.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Imple facies eorum ignominia: et quærent nomen tuum, Domine.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Erubescant, et conturbentur in sæculum sæculi: et confundantur, et pereant.
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Et cognoscant quia nomen tibi Dominus: tu solus Altissimus in omni terra.