< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Canto. Salmo di Asaf. O Dio, non startene cheto; non rimaner muto ed inerte, o Dio!
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Poiché, ecco, i tuoi nemici si agitano rumorosamente, e quelli che t’odiano alzano il capo.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Tramano astuti disegni contro il tuo popolo, e si concertano contro quelli che tu nascondi presso di te.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Dicono: Venite, distruggiamoli come nazione, e il nome d’Israele non sia più ricordato.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Poiché si son concertati con uno stesso sentimento, fanno un patto contro di te:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
le tende di Edom e gl’Ismaeliti; Moab e gli Hagareni;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Ghebal, Ammon ed Amalek; la Filistia con gli abitanti di Tiro;
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
anche l’Assiria s’è aggiunta a loro; prestano il loro braccio ai figliuoli di Lot. (Sela)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Fa’ a loro come facesti a Midian, a Sisera, a Jabin presso al torrente di Chison,
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
i quali furon distrutti a Endor, e serviron di letame alla terra.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Rendi i loro capi simili ad Oreb e Zeeb, e tutti i loro principi simili a Zeba e Tsalmunna;
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
poiché dicono: Impossessiamoci delle dimore di Dio.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Dio mio, rendili simili al turbine, simili a stoppia dinanzi al vento.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Come il fuoco brucia la foresta, e come la fiamma incendia i monti,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
così perseguitali con la tua tempesta, e spaventali col tuo uragano.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Cuopri la loro faccia di vituperio, onde cerchino il tuo nome, o Eterno!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Siano svergognati e costernati in perpetuo, siano confusi e periscano!
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
E conoscano che tu, il cui nome e l’Eterno, sei il solo Altissimo sopra tutta la terra.