< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Ein Psalmlied; von Asaph. Bleibe nicht stille, o Gott, schweige nicht und halte nicht inne!
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Denn siehe, deine Feinde toben, und die dich hassen, erheben das Haupt.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Sie machen listige Anschläge wider dein Volk, verabreden sich wider deine Schutzbefohlenen.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Sie sprechen: «Kommt, wir wollen sie vertilgen, daß sie kein Volk mehr seien, daß des Namens Israel nicht mehr gedacht werde!»
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Ja, sie fassen einen einmütigen Beschluß, sie schließen einen Bund wider dich;
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
die Zelte Edoms und die Ismaeliter, Moab und die Hagariter;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal, Ammon und Amalek, die Philister samt denen zu Tyrus.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Auch Assur hat sich mit ihnen befreundet und leiht den Kindern Lots seinen Arm. (Pause)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Tue ihnen wie Midian, wie Sisera, wie Jabin am Bach Kison,
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
die vertilgt wurden zu Endor, zu Dünger wurden fürs Ackerfeld.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Mache ihre Edlen wie Oreb und Seb, wie Sebach und Zalmuna alle ihre Fürsten,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
die da sagen: «Wir wollen die Wohnstätten Gottes für uns erobern!»
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
O Gott, setze sie dem Wirbelsturm aus, mache sie wie Stoppeln vor dem Wind;
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
wie ein Feuer, das den Wald verbrennt, und wie eine Flamme, welche die Berge versengt;
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
also verfolge sie mit deinem Wetter und schrecke sie mit deinem Sturm!
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Mache ihr Angesicht voll Schande, daß sie deinen Namen suchen, o HERR!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Laß sie beschämt und abgeschreckt werden für immer, laß sie schamrot werden und umkommen,
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
so daß sie erfahren müssen, daß du, der du HERR heißest, allein der Höchste bist über die ganze Erde!