< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
[Ein Lied, ein Psalm. [Eig. Ein Psalm-Lied] Von Asaph.] Gott, schweige nicht [Eig. sei nicht ruhig, untätig; ] verstumme nicht und sei nicht stille, o Gott [El!]
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Denn siehe, deine Feinde toben, und deine Hasser erheben das Haupt.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Wider dein Volk machen sie listige Anschläge, und beraten sich wider deine Geborgenen. [O. Schützlinge]
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Sie sprechen: Kommet und lasset uns sie vertilgen, daß sie keine Nation mehr seien, daß nicht mehr gedacht werde des Namens Israel!
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Denn sie haben sich beraten mit einmütigem Herzen, sie haben einen Bund wider dich gemacht:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
Die Zelte Edoms und die [O. der] Ismaeliter, Moab und die Hageriter,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal und Ammon und Amalek, Philistäa samt den Bewohnern von Tyrus;
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Auch Assur hat sich ihnen angeschlossen; sie sind zu einem Arm geworden den Söhnen Lots. (Sela)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Tue ihnen wie Midian, wie Sisera, wie Jabin am Bache Kison;
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Die vertilgt wurden zu En-Dor, die dem Erdboden zum Dünger wurden!
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Mache sie, ihre Edlen, wie Oreb und wie Seeb, und wie Sebach und wie Zalmunna alle ihre Herrscher! [Eig. Eingesetzte]
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
Weil sie [O. Welche] gesagt haben: Lasset uns in Besitz nehmen die Wohnungen Gottes!
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Mein Gott, mache sie gleich einem Staubwirbel, gleich Stoppeln vor dem Winde!
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Wie Feuer den Wald verbrennt, und wie eine Flamme die Berge entzündet,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Also verfolge sie mit deinem Wetter, und mit deinem Sturmwinde schrecke sie hinweg!
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Fülle ihr Angesicht mit Schande, damit sie deinen Namen, Jehova, suchen!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Laß sie beschämt und hinweggeschreckt werden für immer, und mit Scham bedeckt werden und umkommen,
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Und erkennen, [O. damit sie erkennen] daß du allein, dessen Name Jehova ist, der Höchste bist über die ganze Erde!