< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Cantique d'Asaph. O Dieu, ne garde pas le silence, ne sois point sourd, ne te tiens pas en repos, ô Dieu!
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Car voici, tes ennemis sont en rumeur, et ceux qui te haïssent, lèvent la tête;
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
ils trament contre ton peuple un astucieux complot, et se concertent contre tes protégés.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Ils disent: « Sus! exterminons-les du milieu des peuples, que le nom d'Israël ne soit plus rappelé désormais! »
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Car ils se concertent d'un commun accord, ils font alliance contre toi:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
ce sont les tentes d'Edom et des Ismaëlites, Moab et les Hagariens,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal et Amman et Amalek, la Philistie avec les habitants de Tyr;
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Assur aussi s'unit à eux, et prête son bras aux enfants de Lot. (Pause)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Traite-les comme Madian, comme Sisera, comme Jabin au torrent de Kison,
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
qui furent défaits à En-Dor, et fumèrent le sol!
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Rends-les, rends leurs princes pareils à Horeb et à Zéeb, et tous leurs rois, à Zébah et Tsalmunah;
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
car ils disent: « Rendons-nous maîtres des demeures de Dieu! »
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Mon Dieu, assimile-les au tourbillon, à la balle livrée au vent,
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
au feu qui dévore la forêt, et à la flamme qui embrase la montagne!
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Ainsi, poursuis-les de ta tempête, et terrifie-les par ton ouragan!
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Couvre leur visage de honte, afin qu'ils s'enquièrent de ton nom, Éternel!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Qu'ils soient confondus et terrifiés pour toujours, et qu'ils périssent avec ignominie!
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
afin qu'ils sachent que ton nom, Etemel, ton nom seul est souverain sur toute la terre.

< Zabura 83 >