< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
O Dieu, ne garde pas le silence! Ne sois pas sourd et ne reste pas dans le repos, ô Dieu!
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Car voici, tes ennemis s'agitent, et ceux qui te haïssent ont levé la tête.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Ils font contre ton peuple d'astucieux complots, et se concertent contre ceux que tu protèges.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Venez, disent-ils, faisons-les disparaître d'entre les nations, et qu'on ne parle plus du nom d'Israël.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Car ils ont conspiré d'un même cœur, ils forment une alliance contre toi;
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
Les tentes d'Édom et les Ismaélites, Moab et les Hagaréniens;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Guébal, Ammon et Amalek, les Philistins avec les habitants de Tyr.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Assur aussi se joint à eux; ils prêtent leur bras aux enfants de Lot. (Sélah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Fais-leur comme à Madian; comme à Sisera, comme à Jabin au torrent de Kisson;
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Qui furent détruits à Endor, et servirent de fumier à la terre.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Rends-les, rends leurs princes semblables à Oreb et à Zéeb; et tous leurs rois à Zébach et à Tsalmuna.
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
Car ils disent: Emparons-nous des demeures de Dieu!
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Mon Dieu, rends-les semblables au tourbillon, au chaume emporté par le vent.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Comme le feu dévore la forêt, comme la flamme embrase les montagnes,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Ainsi poursuis-les de ta tempête, épouvante-les par ton ouragan.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Remplis leur face d'ignominie, et qu'ils cherchent ton nom, ô Éternel!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Qu'ils soient honteux, qu'ils soient épouvantés à jamais, qu'ils soient rendus confus et qu'ils périssent!
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Et qu'ils connaissent que toi seul, qui t'appelles l'Éternel, tu es le souverain de toute la terre.

< Zabura 83 >