< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Cantique et Psaume d'Asaph. Ô Dieu! ne garde point le silence, ne te tais point, et ne te tiens point en repos, [ô Dieu Fort!]
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Car voici, tes ennemis bruient; et ceux qui te haïssent ont levé la tête.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Ils ont consulté finement en secret contre ton peuple, et ils ont tenu conseil contre ceux qui se sont retirés vers toi pour se cacher.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Ils ont dit: venez, et détruisons-les, en sorte qu'ils ne soient plus une nation, et qu'on ne fasse plus mention du nom d'Israël.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Car ils ont consulté ensemble d'un même esprit; ils ont fait alliance contre toi.
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
Les tentes des Iduméens, des Ismaélites, des Moabites, et des Hagaréniens;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
les Guébalites, les Hammonites, les Hamalécites, et les Philistins, avec les habitants de Tyr.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Assur aussi s'est joint avec eux; ils ont servi de bras aux enfants de Lot: (Sélah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Fais-leur comme tu fis à Madian, comme à Sisera, [et] comme à Jabin, auprès du torrent de Kison;
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Qui furent défaits à Hen-dor, et servirent de fumier à la terre.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Fais que les principaux d'entr'eux soient comme Horeb, et comme Zéeb; et que tous leurs Princes soient comme Zébah et Tsalmunah;
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
Parce qu'ils ont dit: conquérons-nous les habitations agréables de Dieu.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Mon Dieu! rends-les semblables à une boule, et au chaume chassé par le vent;
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Comme le feu brûle une forêt, et comme la flamme embrase les montagnes.
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Poursuis-les ainsi par ta tempête, et épouvante-les par ton tourbillon.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Couvre leurs visages d'ignominie, afin qu'on cherche ton Nom, ô Eternel!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Qu'ils soient honteux et épouvantés à jamais, qu'ils rougissent, et qu'ils périssent;
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Afin qu'on connaisse que toi seul, qui as nom l’Eternel, es Souverain sur toute la terre.

< Zabura 83 >