< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Cantique. Psaume d’Assaph. O Dieu, n’arrête plus ton action, ne garde pas le silence, ne reste pas en repos, ô Tout-Puissant!
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Car voilà tes ennemis qui s’agitent en tumulte, et tes adversaires qui lèvent la tête.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Contre ton peuple ils ourdissent des complots; ils se concertent contre ceux que tu protèges.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Ils disent: "Allons, rayons-les du nombre des nations; que le nom d’Israël ne soit plus mentionné!"
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Car, d’un commun accord, ils prennent des résolutions, contre toi ils font un pacte:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
les tentes d’Edom et les Ismaélites, Moabites et Hagrites,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Ghebal, Ammon et Amalec, les Philistins ainsi que les habitants de Tyr;
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Achour aussi se joint à eux; ils prêtent main-forte aux fils de Loth. (Sélah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Traite-les comme tu as traité Madian, Sisara et Jabin près du torrent de Kison,
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
qui furent anéantis à Endor, couchés sur le sol comme du fumier.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Rends leur noble pareille à Oreb et à Zeêb, et tous leurs princes, pareils à Zébah et Çalmouna,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
car ils ont dit: "Emparons-nous des demeures de Dieu."
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Mon Dieu, fais d’eux comme un tourbillon de poussière, comme du chaume emporté par le vent.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
De même que le feu dévore les forêts, que la flamme embrase les montagnes,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
ainsi pourchasse-les par ta tempête, jette-les dans une fuite éperdue par ton ouragan.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Couvre leur visage d’opprobre, pour qu’ils recherchent ton nom, ô Eternel.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Qu’ils soient confondus, terrifiés à jamais, saisis de honte et perdus.
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Qu’ils reconnaissent ainsi que toi seul as nom Eternel, que tu es le Maître suprême de toute la terre.

< Zabura 83 >