< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
The song of the salm of Asaph. God, who schal be lijk thee? God, be thou not stille, nether be thou peesid.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
For lo! thin enemyes sowneden; and thei that haten thee reisiden the heed.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Thei maden a wickid counsel on thi puple; and thei thouyten ayens thi seyntis.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
Thei seiden, Come ye, and leese we hem fro the folk; and the name of Israel be no more hadde in mynde.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
For thei thouyten with oon acord;
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
the tabernaclis of Ydumeys, and men of Ismael disposiden a testament togidere ayens thee. Moab, and Agarenus, Jebal, and Amon, and Amalech;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
alienys with hem that dwellen in Tyre.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
For Assur cometh with hem; thei ben maad in to help to the sones of Loth.
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Make thou to hem as to Madian, and Sisara; as to Jabyn in the stronde of Sison.
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Thei perischiden in Endor; thei weren maad as a toord of erthe.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Putte thou the prynces of hem as Oreb and Zeb; and Zebee and Salmana. Alle the princis of hem, that seiden;
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
Holde we bi eritage the seyntuarie of God.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
My God, putte thou hem as a whele; and as stobil bifor the face of the wynde.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
As fier that brenneth a wode; and as flawme brynnynge hillis.
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
So thou schalt pursue hem in thi tempeste; and thou schalt disturble hem in thin ire.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Lord, fille thou the faces of hem with schenschipe; and thei schulen seke thi name.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Be thei aschamed, and be thei disturblid in to world of world; and be thei schent and perische thei.
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
And knowe thei, that the Lord is name to thee; thou aloone art the hiyeste in ech lond.

< Zabura 83 >