< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
A song. A psalm of Asaph. God, do not be silent! Do not ignore us and remain unmoved, God.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Look, your enemies are making a commotion, and those who hate you have raised their heads.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
They conspire against your people and plan together against your protected ones.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
They have said, “Come, and let us destroy them as a nation. Then the name of Israel will no longer be remembered.”
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
They have schemed together with one strategy; against you they have made an alliance.
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
This includes the tents of Edom and the Ishmaelites, and the people of Moab and the Hagrites, who plot together with
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal, Ammon, Amalek; it also includes Philistia and the inhabitants of Tyre.
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Assyria also is allied with them; they are helping the descendants of Lot. (Selah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Do to them as you did to Midian, as you did to Sisera and to Jabin at the Kishon River.
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
They perished at Endor and became like manure for the earth.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Make their nobles like Oreb and Zeeb, and all their princes like Zebah and Zalmunna.
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
They said, “Let us take for ourselves the pastures of God.”
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
My God, make them like the whirling dust, like chaff before the wind,
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
like the fire that burns the forest, and like the flame that sets the mountains on fire.
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Chase them with your strong wind, and terrify them with your windstorm.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Fill their faces with shame so that they might seek your name, Yahweh.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
May they be put to shame and be terrified forever; may they perish in disgrace.
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Then they will know that you alone, Yahweh, are the Most High over all the earth.

< Zabura 83 >