< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
“A song or psalm of Assaph.” O God, take no rest for thyself: be not silent and keep not still, O God!
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
For, lo, thy enemies make a tumult, and they that hate thee have lifted up their head.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Against thy people they take crafty secret device, and they consult against those whom thou protectest.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
They have said, Come, and let us cut them off from being a nation; and the name of Israel shall be remembered no more.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
For they have consulted cordially together; against thee they make a covenant:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
The tents of Edom, and the Ishmaelites: Moab, and the Hagarenes;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal, and 'Ammon, and 'Amalek; the Philistines with the inhabitants of Tyre;
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Also Asshur is joined with them; they have become an arm unto the children of Lot. (Selah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Do unto them as [unto] Midian; as to Sissera, as to Jabin, at the brook Kishon:
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Who were annihilated at 'En-dor; they became as dung for the ground.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Render them, their nobles, like 'Oreb, and like Zeeb; yea, like Zebach and like Zalmunna' all their princes;
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
Who said, Let us conquer for ourselves the dwellings of God,
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
O my God, render them like the thistle-down, like stubble before the wind.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
As the fire burneth up a forest, and as the flame setteth the mountains on fire:
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
So pursue them with thy storm, and with thy whirlwind do thou terrify them.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Fill their faces with shame, that they may seek thy name, O Lord!
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Let them be made ashamed and terrified for ever and aye; yea, let them be put to the blush and perish:
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
That they may know that thou, whose name is the Eternal, art by thyself alone, the Most High over all the earth.