< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
A Song; a Psalm of Asaph. O God, keep not silence; hold not thy peace, and be not still, O God:
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
For behold, thine enemies make a tumult; and they that hate thee lift up the head.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
They take crafty counsel against thy people, and consult against thy hidden ones:
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
They say, Come, and let us cut them off from being a nation, and let the name of Israel be mentioned no more.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
For they have consulted together with one heart: they have made an alliance together against thee.
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
The tents of Edom and the Ishmaelites, Moab and the Hagarites;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal, and Ammon, and Amalek; Philistia, with the inhabitants of Tyre;
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Asshur also is joined with them: they are an arm to the sons of Lot. (Selah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Do unto them as to Midian; as to Sisera, as to Jabin, at the torrent of Kishon:
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Who were destroyed at Endor; they became as dung for the ground.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Make their nobles as Oreb and as Zeeb; and all their chiefs as Zebah and as Zalmunna.
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
For they have said, Let us take to ourselves God's dwelling-places in possession.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
O my God, make them like a whirling thing, like stubble before the wind.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
As fire burneth a forest, and as the flame setteth the mountains on fire,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
So pursue them with thy tempest, and terrify them with thy whirlwind.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Fill their faces with shame, that they may seek thy name, O Jehovah.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Let them be put to shame and be dismayed for ever, and let them be confounded and perish:
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
That they may know that thou alone, whose name is Jehovah, art the Most High over all the earth.

< Zabura 83 >