< Zabura 83 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Een lied; een psalm van Asaf. O God, houd U niet stil, Niet rustig en werkeloos, o God!
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Want zie, uw vijanden razen, En uw haters steken hun hoofden omhoog.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Ze smeden listige plannen tegen uw volk, En spannen tegen uw beschermelingen samen:
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
"Komt, laat ons ze uitroeien uit de rij van de volken, Zodat men zelfs Israëls naam niet meer noemt!"
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Ja, eensgezind hebben ze samengezworen, En een verbond gesloten tegen U:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
De tenten van Edom en van de Jisjmaëlieten, Van Moab en de zonen van Hagar.
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
En Gebal, Ammon en Amalek, Filistea met de bewoners van Tyrus,
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Zelfs Assjoer sluit zich bij hen aan, En leent zijn arm aan de zonen van Lot.
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Doe met hen als met Midjan, Als met Sisera en Jabin bij de beek Kisjon,
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Die bij En-Dor werden vernietigd, En tot mest voor het veld zijn gemaakt.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Zet het hun vorsten betaald als Oreb en Zeëb, Als Zébach en Salmoenna,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
Met al hun groten, die zeggen: Laat ons het land van God gaan bezetten!
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Maak ze aan dwarrelende blaren gelijk, o mijn God, En aan kaf voor de wind!
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
En zoals het vuur de bossen verteert, De vlammen de bergen verzengen:
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Zo moogt Gij hen met uw stormwind vervolgen, In verwarring brengen door uw orkaan!
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Bedek met smaad hun gelaat, Opdat ze uw Naam mogen eren, o Jahweh;
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Laat ze beschaamd staan en verbijsterd voor eeuwig, En in schande vergaan!
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Dan zullen zij weten, dat "Jahweh" uw Naam is; Dat Gij de Allerhoogste zijt op heel de aarde, Gij alleen!

< Zabura 83 >