< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
En Sang. En Salme af Asaf.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Und dig, o Gud, ikke Ro, vær ej tavs, vær ej stille, o Gud!
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Thi se, dine Fjender larmer, dine Avindsmænd løfter Hovedet,
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
oplægger lumske Raad mod dit Folk, holder Raad imod dem, du værner:
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
»Kom, lad os slette dem ud af Folkenes Tal, ej mer skal man ihukomme Israels Navn!«
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
Ja, de raadslaar i Fællig og slutter Pagt imod dig,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Edoms Telte og Ismaeliterne, Moab sammen med Hagriterne,
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Gebal, Ammon, Amalek, Filisterland med Tyrus's Borgere;
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
ogsaa Assur har sluttet sig til dem, Lots Sønner blev de en Arm. (Sela)
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
Gør med dem som med Midjan, som med Sisera og Jabin ved Kisjons Bæk,
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
der gik til Grunde ved En-Dor og blev til Gødning paa Marken!
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
Deres Høvdinger gaa det som Oreb og Ze'eb, alle deres Fyrster som Zeba og Zalmunna,
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
fordi de siger: »Guds Vange tager vi til os som Eje.«
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Min Gud, lad dem blive som hvirvlende Løv, som Straa, der flyver for Vinden.
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
Ligesom Ild fortærer Krat og Luen afsvider Bjerge,
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
saa forfølge du dem med din Storm, forfærde du dem med din Hvirvelvind;
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
fyld deres Aasyn med Skam, saa de søger dit Navn, o HERRE;
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
lad dem blues, forfærdes for stedse, beskæmmes og gaa til Grunde Og kende, at du, hvis Navn er HERREN, er ene den Højeste over al Jorden!