< Zabura 82 >

1 Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
Dios está en la congregación de Dios; en medio de los dioses juzga.
2 “Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
¿Hasta cuándo juzgaréis injustamente: y aceptaréis las personas de los impíos? (Selah)
3 Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
Hacéd derecho al pobre y al huérfano: justificád al afligido y al menesteroso.
4 Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Librád al afligido y al menesteroso: librádle de mano de los impíos.
5 “Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
No saben, no entienden: andan en tinieblas, vacilan todos los cimientos de la tierra.
6 “Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
Yo dije, dioses sois vosotros; y todos vosotros hijos del Altísimo.
7 Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
Empero como hombres moriréis: y como cualquiera de los tiranos caeréis.
8 Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.
Levántate o! Dios, juzga la tierra: porque tú heredarás en todas las naciones.

< Zabura 82 >