< Zabura 82 >

1 Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
Un salmo de Asaf. Dios permanece en medio de su gran asamblea para juzgar a los que juzgan.
2 “Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
¿Hasta cuándo juzgarán injustamente y mostrarán favoritismo hacia los malvados? (Selah)
3 Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
Defiendan a los pobres y a los huérfanos; apoyen los derechos de los que son oprimidos y están sufriendo.
4 Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Rescaten al pobre y a aquellos que no pueden ayudarse a sí mismos; sálvenlos de las garras de los malvados.
5 “Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
Estos jueces no tienen nada de sabiduría; viven en la oscuridad; los cimientos de la tierra son sacudidos.
6 “Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
Yo digo, “Ustedes son jueces; todos ustedes son hijos del Altísimo.
7 Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
Pero morirán como cualquier ser humano, caerán como cualquier otro líder”.
8 Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.
Levántate, Señor, y juzga la tierra, porque todas las naciones te pertenecen a ti.

< Zabura 82 >