< Zabura 82 >
1 Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
A psalm of Asaph God [is] taking his stand in [the] congregation of God in [the] midst of [the] gods he gives judgment.
2 “Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
Until when? will you judge injustice and [the] face of wicked [people] will you lift up (Selah)
3 Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
Give judgment for [the] poor and [the] fatherless [the] afflicted and [the] poor vindicate.
4 Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Deliver [the] poor and [the] needy from [the] hand of wicked [people] rescue [them].
5 “Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
Not they know - and not they understand in darkness they walk about they are shaken all [the] foundations of [the] earth.
6 “Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
I I said [are] gods you and [are] [the] children of [the] Most High all of you.
7 Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
Nevertheless like humankind you will die! and like one of the princes you will fall.
8 Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.
Arise! O God judge! the earth for you you have an inheritance among all the nations.