< Zabura 82 >
1 Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
“A psalm of Asaph.” God standeth in God's assembly, He judgeth in the midst of the gods.
2 “Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
“How long will ye judge unjustly, And favor the cause of the wicked? (Pause)
3 Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
Defend the poor and the fatherless; Do justice to the wretched and the needy!
4 Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Deliver the poor and the destitute; Save them from the hand of the wicked!
5 “Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
They are without knowledge and without understanding; They walk in darkness: Therefore all the foundations of the land are shaken.
6 “Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
I have said, Ye are gods, And all of you children of the Most High;
7 Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
But ye shall die like men, And fall like the rest of the princes.”
8 Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.
Arise, O God! judge the earth! For all the nations are thy possession.