< Zabura 82 >

1 Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
GOD standeth in the congregation of the mighty; he judgeth among the gods.
2 “Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
How long will ye judge unjustly, and accept the persons of the wicked? (Selah)
3 Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
Defend the poor and fatherless: do justice to the afflicted and needy.
4 Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Deliver the poor and needy: rid them out of the hand of the wicked.
5 “Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
They know not, neither will they understand; they walk on in darkness: all the foundations of the earth are out of course.
6 “Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
I have said, Ye are gods; and all of you are children of the most High.
7 Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
But ye shall die like men, and fall like one of the princes.
8 Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.
Arise, O God, judge the earth: for thou shalt inherit all nations.

< Zabura 82 >