< Zabura 82 >

1 Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”. 2 “Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela) 3 Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya. 4 Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye. 5 “Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya. 6 “Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne. 7 Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.” 8 Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.

< Zabura 82 >