< Zabura 81 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Para el músico principal. En un instrumento de Gath. Por Asaf. ¡Canta en voz alta a Dios, nuestra fuerza! ¡Haz un grito de júbilo al Dios de Jacob!
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Eleva una canción, y trae aquí la pandereta, la agradable lira con el arpa.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Toca la trompeta en la Luna Nueva, en la luna llena, en nuestro día de fiesta.
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Porque es un estatuto para Israel, una ordenanza del Dios de Jacob.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Lo designó en José para un pacto, cuando salió sobre la tierra de Egipto, Oí un idioma que no conocía.
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
“Quité su hombro de la carga. Sus manos se liberaron de la cesta.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Llamaste a la angustia, y te libré. Te respondí en el lugar secreto del trueno. Te probé en las aguas de Meribah”. (Selah)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
“Oíd, pueblo mío, y yo os daré testimonio, ¡Israel, si me escuchas!
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
No habrá en ti ningún dios extraño, ni adorarás a ningún dios extranjero.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Yo soy Yahvé, tu Dios, que te sacó de la tierra de Egipto. Abre bien tu boca y la llenaré.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Pero mi pueblo no escuchó mi voz. Israel no deseaba nada de mí.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Así que los dejé ir tras la terquedad de sus corazones, para que puedan caminar en sus propios consejos.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Oh, que mi pueblo me escuche, para que Israel siga mis caminos.
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
Pronto sometería a sus enemigos, y volver mi mano contra sus adversarios.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Los que odian a Yahvé se acobardan ante él, y su castigo duraría para siempre.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Pero también los habría alimentado con lo más fino del trigo. Te saciaré con miel de la roca”.