< Zabura 81 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Para el director del coro. En el gitit. Un salmo de Asaf. Canten a Dios, porque es nuestra fuerza; griten de alegría al Dios de Jacob.
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
¡Comiencen la canción! Toquen la pandereta, la lira de sonido dulce, y el arpa.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Soplen la trompeta a la luna nueva, y a la luna llena, para iniciar nuestros festivales,
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
porque esta es una regla de Israel, un reglamento del Dios de Jacob.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Dios hizo este estatuto por José, cuando se opuso a la tierra de Egipto. Escuché una voz que no conocía diciendo:
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
“Tomo la carga de tus hombros; libero tus manos de las canastas pesadas.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Clamaste a mí en tu sufrimiento, y te salvé. Te respondí desde las nubes tormentosas. Te probé en las aguas de Meriba. (Selah)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
¡Pueblo mío! ¡Escuchen mis avisos! Pueblo de Israel, ¡Escúchenme!
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
No debe haber dios extraño entre ustedes; no deben postrarse nunca ante dioses extranjeros ni adorarlos.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Porque yo soy el Señor su Dios que los sacó de la tierra de Egipto. Abran su boca y yo los saciaré.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Pero mi pueblo no me escuchó. Israel no quería nada conmigo.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Así que los envié lejos a seguir su pensamiento terco, viviendo como escogieran.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
¡Si tan solo mi pueblo me escuchara; si tan solo Israel siguiera mis caminos!
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
No me tomaría tanto tiempo derrotar a sus enemigos, ni derribar a los que están en su contra.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Los que odian al Señor se retorcerán frente a él, condenados para siempre.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Pero yo, los alimentaría con el mejor trigo, y los satisfaría con miel de la roca”.